6 Su yi girma har su yi huda,Sa'an nan su yi yaushi su bushe da yamma.
7 Mun halaka ta wurin fushinka,Mun razana saboda hasalarka.
8 Ka jera zunubanmu a gabanka,Zunubanmu na ɓoye kuwa,Ka sa su a inda za ka gan su.
9 Fushinka ya gajerta tsawon ranmu,Ranmu ya ƙare kamar ajiyar zuciya.
10 Tsawon kwanakin ranmu duka a ƙalla shekara ce saba'in,In kuwa muna da ƙarfi, shekara tamanin ne.Duk da haka iyakar abin da waɗannan shekaruSuke kawo mana, damuwa ce da wahala,Nan da nan sukan wuce,Tamu da ƙare.
11 Wa ya san iyakar ikon fushinka?Wa ya san irin tsoron da hasalarka za ta kawo?
12 Ka koya mana mu sani ranmu na ɗan lokaci ne,Domin mu zama masu hikima.