1 Duk wanda ya je wurin MaɗaukakiZai zauna lafiya,Duk wanda yake zaune a inuwar Mai Iko Dukka,
2 Ya iya ce wa Ubangiji,“Kai ne kāriyata, da mai kiyaye ni!Kai ne Allahna, a gare ka nake dogara!”
3 Hakika zai kiyaye kaDaga dukan hatsarorin da ka ɓoye,Daga kuma dukan mugayen cuce-cuce.
4 Zai rufe ka da fikafikansa,Za ka zauna lafiya a ƙarƙashinsu.Amincinsa zai tsare ka, ya kiyaye ka.
5 Ba za ka ji tsoron hatsarori da dare ba,Ko fāɗawar da za a yi maka da rana,