7 Mutum dubu za su fāɗi daura da kai,Dubu goma kuma za su fāɗi dama da kai,Amma kai, ba za a cuce ka ba.
8 Da idonka za ka duba, Ka ga yadda ake hukunta wa mugaye.
9 Domin ka ɗauka Ubangiji yake kiyaye ka,Maɗaukaki ne yake tsaronka,
10 To, ba bala'in da zai same ka,Ba za a yi wa gidanka aikin ƙarfi da yaji ba.
11 Allah zai sa mala'ikunsa su lura da kai,Za su kiyaye ka duk inda za ka tafi.
12 Za su ɗauke ka a hannuwansu,Don kada ka buga ƙafarka a dutse.
13 Za ka tattake zakoki da macizai,Za ka tattake zakoki masu zafin raiDa macizai masu dafi.