7 Shi ne mai yiwuwa ne mugu ya yi girma kamar tsire-tsire,Masu aikata mugayen ayyuka kuma su arzuta,Duk da haka za a hallaka su ɗungum.
8 Gama kai, ya Ubangiji,Maɗaukaki ne har abada.
9 Mun sani maƙiyanka za su mutu,Dukan mugaye kuwa za a yi nasara da su.
10 Ka sa ni na yi ƙarfi kamar bijimi mai faɗa,Ka sa mini albarka da farin ciki.
11 Na ga fāɗuwar maƙiyana,Na ji kukan mugaye.
12 Adalai za su yi yabanyaKamar itatuwan giginya,Za su yi girma kamar itatuwan al'ul na Lebanon.
13 Za su zama kamar itatuwan da aka daddasa a Haikalin Ubangiji,Suna ta yabanya a Haikalin Allahnmu.