7 Suna cewa, “Ai, Ubangiji ba ya ganinmu,Allah na Isra'ila ba ya lura da abin da yake faruwa!”
8 Ya jama'ata, ƙaƙa kuka zama dakikai, wawaye haka?Sai yaushe za ku koya?
9 Allah ya yi mana kunnuwa, shi ba zai ji ba?Allah ya yi mana idanu, shi ba zai gani ba?
10 Shi ne yake shugabancin sauran al'umma, ba zai hukunta su ba?Shi ne yake koya wa dukan mutane, shi ba shi da sani ne?
11 Ubangiji ya san tunaninsu,Ya san kuma hujjojinsu na rashin hankali.
12 Ya Ubangiji, mai farin ciki ne mutumin da kake koya wa,Mutumin da kake koya masa shari'arka.
13 Don ka ba shi hutawa a kwanakin wahala,Kafin a haƙa wa mugaye kabari.