9 Allah ya yi mana kunnuwa, shi ba zai ji ba?Allah ya yi mana idanu, shi ba zai gani ba?
10 Shi ne yake shugabancin sauran al'umma, ba zai hukunta su ba?Shi ne yake koya wa dukan mutane, shi ba shi da sani ne?
11 Ubangiji ya san tunaninsu,Ya san kuma hujjojinsu na rashin hankali.
12 Ya Ubangiji, mai farin ciki ne mutumin da kake koya wa,Mutumin da kake koya masa shari'arka.
13 Don ka ba shi hutawa a kwanakin wahala,Kafin a haƙa wa mugaye kabari.
14 Ubangiji ba zai rabu da jama'arsa ba,Ba zai rabu da waɗanda suke nasa ba.
15 Adalci kuma zai sāke dawowa cikin majalisun alƙalai,Dukan adalai kuwa za su yi na'am da shi.