28 Ka ba su, sun ci,Ka tanada musu abinci, sun ƙoshi.
29 Sa'ad da ka rabu da su sukan tsorata,In ka zare numfashin da ka ba su, sai su mutu,Su koma turɓaya, da ma da ita aka yi su.
30 Amma sa'ad da ka hura musu numfashi, sai su rayu,Kakan sabunta fuskar duniya.
31 Da ma darajar Ubangiji ta dawwama har abada!Da ma Ubangiji ya yi farin ciki da abin da ya halitta!
32 Ya dubi duniya, sai ta girgiza,Ya taɓa duwatsu, sai suka tuɗaɗo da hayaƙi.
33 Zan raira waƙa ga Ubangiji dukan raina,Zan raira yabbai ga Allah muddin raina.
34 Da ma ya ji daɗin waƙata,Saboda yakan sa ni in yi murna.