1 A cikin fid da zuciyata,Na yi kira gare ka, ya Ubangiji.
2 Ka ji kukana, ya Ubangiji,Ka kasa kunne ga kiran da nake yi na neman taimako!
3 Idan kana yin lissafin zunubanmu,Wa zai kuɓuta daga hukunci?
4 Amma kakan gafarta mana,Domin mu zama masu tsoronka.