8 Ka zo wurin hutawarka, ya Ubangiji,Tare da akwatin alkawari,Alama ce ta ikonka.
9 Ka suturta firistoci da adalci,Ka sa dukan jama'arka su yi sowa ta farin ciki!
10 Ka yi wa bawanka Dawuda alkawari,Kada ka rabu da zaɓaɓɓen sarkinka, ya Ubangiji!
11 Ka yi wa Dawuda muhimmin alkawari,Ba kuwa za ka ta da alkawarin ba.Ka ce, “Za naɗa ɗaya daga cikin 'ya'yanka maza yă zama sarki,Zai yi mulki a bayanka.
12 Idan 'ya'yanka maza za su amince da alkawarina,Da umarnan da na yi musu,'Ya'yansu maza kuma za su bi bayanka su zama sarakuna,A dukan lokaci.”
13 Ubangiji ya yaɓi Sihiyona,A can yake so ya gina Haikalinsa, ya ce,
14 “A nan zan zauna har abada.A nan kuma nake so in yi mulki.