5 Za su raira waƙa a kan abin da Ubangiji ya yi,Za su raira waƙa kuma a kan ɗaukakarsa mai girma.
6 Ko da yake Ubangiji yana can Sama,Duk da haka yana kulawa da masu kaɗaici.Masu girmankai kuwa ba za su iya ɓoye kansu daga gare shi ba.
7 Ko lokacin da nake tsakiyar wahala,Za ka kiyaye ni lafiya,Ka yi gāba da abokan gābana, waɗanda suka husata,Za ka kuwa cece ni da ikonka.
8 Za ka aikata kowane abu da ka alkawarta mini,Ya Ubangiji, ƙaunarka madawwamiya ce har abada.Ka cikasa aikin da ka fara.