1 Ya Ubangiji ka ji addu'ata,Ka kasa kunne ga roƙona!Kai adali ne mai aminci,Don haka ka amsa mini!
2 Ni bawanka, kada ka gabatar da ni a gaban shari'a,Gama ba wanda ba shi da laifi a gare ka.
3 Maƙiyina ya tsananta mini,Ya kore ni fata-fata.Ya sa ni a kurkuku mai duhu,Ina kama da waɗanda suka daɗe da mutuwa,
4 Don haka ina niyya in fid da zuciya,Ina cikin damuwa mai zurfi.
5 Na tuna kwanakin baya,Na tuna da dukan abin da ka yi,Na tuna da dukan ayyukanka.
6 Na ɗaga hannuwana sama, ina addu'a gare ka,Kamar busasshiyar ƙasa, raina yana jin ƙishinka.