9 Na tafi wurinka don ka kiyaye ni, ya Ubangiji,Ka cece ni daga maƙiyana.
10 Kai ne Allahna,Ka koya mini in aikata nufinka.Ka sa in sami alherin Ruhunka.Ka bi da ni a hanyar lafiya.
11 Ka cece ni, ya Ubangiji, kamar yadda ka alkawarta.Saboda alherinka ka tsamo ni daga wahalaina!
12 Saboda ƙaunar da kake yi mini,Ka kashe maƙiyana.Ka hallakar da dukan waɗanda suke zaluntata.Gama ni bawanka ne.