11 Suna ba ni ilimi, ni baranka,Ina samun ladan yin biyayya da su.
12 Ba mai iya ganin kuskuren kansa,Ka cece ni daga ɓoyayyun laifofi!
13 Ka tsare ni kuma daga laifofi na fili,Kada ka bari su mallake ni.Sa'an nan zan zama kamili,In kuɓuta daga mugun zunubi.
14 Ka sa maganata da tunanina su zama abin karɓa a gare ka,Ya Ubangiji, Mafakata da Mai Fansata!