8 Suka ce, “Ka dogara ga Ubangiji,Me ya sa bai cece ka ba?Idan Ubangiji na sonka,Don me bai taimake ka ba?”
9 Kai ne ka fito da ni lafiya a lokacin da aka haife ni,A lokacin da nake jariri ka kiyaye ni.
10 Tun daga lokacin da aka haife ni nake dogara gare ka,Kai ne Allahna tun daga ran da aka haife ni.
11 Kada ka yi nisa da ni!Wahala ta gabato,Ba kuwa mai taimako.
12 Magabta da yawa sun kewaye ni kamar bijimai,Dukansu suna kewaye da ni,Kamar bijimai masu faɗa na ƙasar Bashan.
13 Sun buɗe bakinsu kamar zakoki,Suna ruri, suna ta bina a guje.
14 Ƙarfina ya ƙare,Ya rabu da ni kamar ruwan da ya zube ƙasa.Dukan gaɓoɓina sun guggulle,Zuciyata ta narke kamar narkakken kakin zuma.