3 Madawwamiyar ƙaunarka tana bi da ni,Amincinka yake yi mini jagora kullayaumin.
4 Ba na tarayya da mutanen banza,Ba abin da ya gama ni da masu riya.
5 Ina ƙin tarayya da masu mugunta,Nakan kauce wa mugaye.
6 Ya Ubangiji, na wanke hannuwanaDon in nuna ba ni da laifi,Da ibada nakan taka, ina kewaya bagadenka.
7 Na raira waƙar godiya,Na faɗi dukan ayyukanka masu banmamaki.
8 Ya Ubangiji, ina ƙaunar Haikali inda zatinka yake,Inda ɗaukakarka yake zaune.
9 Kada ka hallaka ni tare da masu zunubi,Ka cece ni daga ƙaddarar masu kisankai,