7 Muryar Ubangiji ta sa walƙiya ta walƙata.
8 Muryarsa ta sa hamada ta girgiza,Ta girgiza hamadar Kadesh.
9 Muryar Ubangiji ta sa barewa ta haihu,Ta sa itatuwa su kakkaɓe,Sa'ad da aka yi sowa a cikin Haikalinsa,Aka ce, “Daukaka ga Allah!”
10 Ubangiji yana sarautar ruwa mai zurfi,Yana sarauta kamar sarki har abada.
11 Ubangiji yana ba jama'arsa ƙarfi,Ya sa musu albarka da salama.