3 Kai ne mafakata da kariyata,Ka bi da ni yadda ka alkawarta.
4 Ka kiyaye ni daga tarkon da aka kafa domina,Kai ne inuwata.
5 Ina ba da kaina gare ka domin ka kiyaye ni.Za ka fanshe ni, ya Ubangiji,Kai Allah mai aminci ne.
6 Kana ƙin waɗanda suke yi wa gumaka sujada,Amma ni na dogara gare ka.
7 Zan yi murna da farin ciki,Saboda madawwamiyar ƙaunarka.Ka ga wahalata,Ka kuwa san damuwata.
8 Ba ka bar magabtana su kama ni ba,Ka kiyaye ni.
9 Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji,Gama ina shan wahala,Idanuna sun gaji saboda yawan kuka,Na kuwa tafke ƙwarai!