14 Kamar yadda zan yi wa aboki ko ɗan'uwa addu'a.Ina tafe a takure saboda makoki,Kamar wanda yake makoki domin mahaifiyarsa.
15 Sa'ad da nake shan wahala,Murna suke yi duka,Sun kewaye ni, suna ta yi mini dariya,Baƙi sun duke ni, suna ta buguna.
16 Suka wahalshe ni, suka yi mini dariya,Suna hararata da ƙiyayya.
17 Sai yaushe, za ka duba, ya Ubangiji?Ka kuɓutar da ni daga farmakinsu,Ka ceci raina daga waɗannan zakoki!
18 Sa'an nan zan yi maka godiya a gaban babban taron jama'a.Zan yabe ka a gaban babban taro.
19 Kada ka bar maƙiyana, maƙaryatan nan, su ga fāɗuwata!Kada ka bar waɗanda suke ƙina ba dalili,Su ƙyaface ni, su yi murna saboda baƙin cikina!
20 Ba su yin maganar zumunci,A maimakon haka sukan ƙaga ƙarairayi a kan masu ƙaunar limana.