20 Ba su yin maganar zumunci,A maimakon haka sukan ƙaga ƙarairayi a kan masu ƙaunar limana.
21 Sukan zarge ni da kakkausan harshe,Su ce, “Mun ga abin da ka yi!”
22 Amma kai, ya Ubangiji ka ga wannan.Saboda haka kada ka ƙyale su, ya Ubangiji,Kada ka yi nisa!
23 Ka tashi, ya Ubangiji, ka kāre ni.Ya Allah ka tashi, ka bi mini hakkina.
24 Kai mai adalci ne, ya Ubangiji, ka shaida rashin laifina,Kada ka bar maƙiyana su ƙyaface ni, ya Allahna!
25 Kada ka bar su su ce wa kansu,“Madalla! Da ma abin da muke so ke nan!”Kada ka bar su su ce,“Mun rinjaye shi!”
26 Ka sa waɗanda suka ƙyaface ni a wahalata,A rinjaye su, su ruɗe.Ka sa waɗanda suke ɗaukar kansu sun fi ni,Su sha kunya da wulakanci!