8 Amma kafin su farga, hallaka za ta kama su.Tarkunan da suka kafa za su kama su,Su kuma fāɗa cikin ramin da suka haƙa!
9 Sa'an nan zan yi murna saboda Ubangiji,Zan yi murna, gama ya cece ni.
10 Da zuciya ɗaya zan ce wa Ubangiji,“Ba wani kamarka!Kakan kāre marasa ƙarfi daga masu ƙarfi,Talaka da matalauci kuma daga azzalumai!”
11 Mugaye suna ba da muguwar shaida a kaina,Suna kai ƙarata a kan laifofin da ban san kome a kansa ba.
12 Sun sāka mini alheri da mugunta,Cike nake da nadama.
13 Amma sa'ad da suke ciwo, nakan sa tufafin makoki,Na ƙi cin abinci,Na yi addu'a da kaina a sunkuye,
14 Kamar yadda zan yi wa aboki ko ɗan'uwa addu'a.Ina tafe a takure saboda makoki,Kamar wanda yake makoki domin mahaifiyarsa.