20 Amma mugaye za su mutu,Magabtan Ubangiji kuwa za su shuɗe kamar furen jeji,Za su ɓace kamar hayaƙi.
21 Mugu yakan ci bashi, yă ƙi biya,Amma mutumin kirki mai alheri ne,Mai bayarwa hannu sake.
22 Waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka,Za su zauna lafiya lau a ƙasar,Amma waɗanda ya la'antaZa a kore su su fita.
23 Ubangiji yakan bi da mutum lafiyaA hanyar da ya kamata yă bi,Yakan ji daɗin halinsa,
24 In ya fāɗi, ba zai yi warwar ba,Gama Ubangiji zai taimake shiYă tashi tsaye.
25 Yanzu dai na tsufa, ni ba yaro ba ne,Amma ban taɓa ganin Ubangiji ya yar da mutumin kirki ba,Ko kuma a ga 'ya'yansa suna barar abinci.
26 A koyaushe yakan bayar a sake,Yana ba da rance ga waɗansu,'Ya'yansa kuwa dalilin albarka ne.