25 Yanzu dai na tsufa, ni ba yaro ba ne,Amma ban taɓa ganin Ubangiji ya yar da mutumin kirki ba,Ko kuma a ga 'ya'yansa suna barar abinci.
26 A koyaushe yakan bayar a sake,Yana ba da rance ga waɗansu,'Ya'yansa kuwa dalilin albarka ne.
27 Ka rabu da mugunta ka aikata nagarta,Za ka kuwa zauna a ƙasar har abada,
28 Gama Ubangiji yana ƙaunar abin da yake daidai,Ba ya rabuwa da amintattun jama'arsa,Yana kiyaye su koyaushe,Amma za a kori zuriyar mugaye.
29 Adalai za su yi zamansu lafiya a ƙasar,Su gāje ta har abada.
30 Kalmomin mutumin kirki suna da hikima,Yana faɗar abin da yake daidai.
31 Yakan riƙe dokar Allahnsa a zuciyarsa, Ba ya kauce mata, faufau.