28 Gama Ubangiji yana ƙaunar abin da yake daidai,Ba ya rabuwa da amintattun jama'arsa,Yana kiyaye su koyaushe,Amma za a kori zuriyar mugaye.
29 Adalai za su yi zamansu lafiya a ƙasar,Su gāje ta har abada.
30 Kalmomin mutumin kirki suna da hikima,Yana faɗar abin da yake daidai.
31 Yakan riƙe dokar Allahnsa a zuciyarsa, Ba ya kauce mata, faufau.
32 Mugu yakan yi fakon mutumin kirki,Yă yi ƙoƙari yă kashe shi,
33 Amma Ubangiji ba zai bar shi a hannun magabtansa ba,Ko kuwa yă bari a kāshe shiSa'ad da ake masa shari'a.
34 Ka sa zuciyarka ga UbangijiKa kiyaye dokokinsa,Shi zai ba ka ƙarfin da za ka mallaki ƙasar,Za ka kuwa ga an kori mugaye.