29 Adalai za su yi zamansu lafiya a ƙasar,Su gāje ta har abada.
30 Kalmomin mutumin kirki suna da hikima,Yana faɗar abin da yake daidai.
31 Yakan riƙe dokar Allahnsa a zuciyarsa, Ba ya kauce mata, faufau.
32 Mugu yakan yi fakon mutumin kirki,Yă yi ƙoƙari yă kashe shi,
33 Amma Ubangiji ba zai bar shi a hannun magabtansa ba,Ko kuwa yă bari a kāshe shiSa'ad da ake masa shari'a.
34 Ka sa zuciyarka ga UbangijiKa kiyaye dokokinsa,Shi zai ba ka ƙarfin da za ka mallaki ƙasar,Za ka kuwa ga an kori mugaye.
35 Na ga wani mugu, azzalumi,Ya fi kowa tsayi,Kamar itacen al'ul na Lebanon,