1 Na yi ta jiran taimakon Ubangiji,Sa'an nan ya kasa kunne gare ni, ya ji kukana.
2 Ya fisshe ni daga rami mai hatsari!Ya aza ni a kan dutse lafiya lau.Ya kawar mini da tsoro.
3 Ya koya mini raira sabuwar waƙa,Waƙar yabon Allahnmu.Da yawa idan suka ga wannan za su tsorata,Za su kuwa dogara ga Ubangiji.
4 Mai farin ciki ne mutumin da yake dogara ga Ubangiji,Wanda bai juya ga gumaka ba,Ko ya haɗa kai da masu sujada ga allolin karya.