6 Na ce, “Da a ce ina da fikafikai kamar kurciya,Da sai in tashi, in tafi, in nemi wurin hutawa!
7 In tafi can nesa,In yi wurin zamana a hamada.
8 Zan hanzarta in nemi mafakaDaga iska mai ƙarfi da hadiri.”
9 Ka hallaka su, ya Ubangiji, ka birkitar da maganarsu,Gama na ga hargitsi da tawaye a birni.
10 Dare da rana suna ta yawo a kan garu suna ta kewaye birnin,Birnin kuwa cike yake da laifi da wahala.
11 Akwai hallaka a ko'ina,Tituna suna cike da azzalumai da 'yan danfara.
12 Da a ce maƙiyina ne yake mini ba'a,Da sai in jure.Da a ce abokin gābana ne yake shugabancina,Da sai in ɓuya masa.