10 Ina dogara ga Allah, ina yabon alkawarinsa,Ina dogara ga Ubangiji, ina yabon alkawarinsa.
11 A gare shi nake dogara,Ba zan ji tsoro ba.Me mutum kawai zai yi mini?
12 Zan miƙa maka abin da na yi alkawari, ya Allah,Zan miƙa maka hadaya ta godiya.
13 Domin ka cece ni daga mutuwa,Ka hana a ci nasara a kaina.Saboda haka a gaban Allah nake tafiyaA hasken da yake haskaka wa masu rai.