23 Don ku wanke sawayenku a cikin jinin maƙiyanku,Karnukanku kuwa za su lashe iyakar abin da suke so.”
24 Ya Allah, jama'a duka sun ga irin tafiyarka ta nasara,Irin tafiyar Allah, Sarkina, zuwa tsattsarkan wurinsa.
25 Mawaƙa suna kan gaba, mabusa suna biye,A tsakiya kuwa 'yan mata suna kaɗa bandiri.
26 “Ku jama'ar Allah, ku yabe shi cikin taronku,Ku yabi Ubangiji, dukanku, ku zuriyar Isra'ila!”
27 Ga Biliyaminu mafi ƙanƙantaCikin kabilai, a kan gaba,Sa'an nan shugabannin Yahuza da ƙungiyarsu,Daga nan sai shugabannin Zabaluna da na Naftali suna biye da su.
28 Ka nuna ikonka, ya Allah,Ikon nan da ka nuna saboda mu.
29 Daga Haikalinka a Urushalima,Sarakuna sukan kawo maka kyautai.