1 Ku kasa kunne ga koyarwata, ya ku jama'ata,Ku kula da abin da nake faɗa.
2 Zan yi magana da ku,In faɗa muku asirai na dā,
3 Abubuwan da muka ji muka kuwa sani,Waɗanda kakanninmu suka faɗa mana.
4 Ba za mu ɓoye waɗannan abubuwa daga 'ya'yanmu ba,Amma za mu faɗa wa tsara mai zuwaLabarin ikon Ubangiji, da manya manyan ayyukansa,Da abubuwan banmamaki waɗanda ya aikata.
5 Ya ba da dokoki ga jama'ar Isra'ila,Da umarnai ga zuriyar Yakubu.Ya ba kakanninmu ka'idodi,Don su koya wa 'ya'yansu dokokinsa,
6 Saboda tsara mai zuwa ta koye su,Su kuma su koya wa 'ya'yansu.
7 Ta haka su ma za su dogara ga Allah,Ba za su manta da abin da ya yi ba,Amma a kullum za su riƙa biyayya da umarnansa.