1 Ku yabi Ubangiji!Ku yi wa Ubangiji godiya, gama nagari ne shi,Ƙaunarsa madawwamiya ce.
2 Wa zai iya faɗar dukan manya manyan ayyuka da ya yi?Wa zai iya yi masa isasshen yabo?
3 Masu farin ciki ne waɗanda suke biyayya da umarnansa,Waɗanda kullayaumi suke aikata abin da yake daidai!
4 Ka tuna da ni sa'ad da za ka taimaki jama'arka, ya Ubangiji!Ka sa ni cikinsu, sa'ad da za ka cece su.
5 Ka yardar mini in ga wadatar jama'arka,In yi tarayya da jama'arka da farin cikinsu,In yi farin ciki tare da waɗanda suke murna ta fāriya domin su naka ne.
6 Mun yi zunubi yadda kakanninmu suka yi,Mugaye ne, mun aikata mugunta.
7 Kakanninmu a MasarBa su fahimci ayyukan Allah masu banmamaki ba,Sau da yawa sukan manta da irin ƙaunar da ya nuna musu,Suka tayar wa Mai Iko Dukka a Bahar Maliya.