4 Ubangiji ya ce, “Ba su sani ba?Duk waɗannan masu aikin mugunta jahilai ne?Ta wurin yi wa jama'ata fashi suke zaman gari,Ba su yin addu'a gare ni.”
5 Amma za su razana,Gama Allah yana tare da masu yi masa biyayya.
6 Suna yi wa shirye-shiryen kāsasshe dariya,Saboda yana dogara ga Ubangiji.
7 Ina addu'a matuƙa domin ceto ya zo ga Isra'ila daga Sihiyona!Sa'ad da Ubangiji ya sāke arzuta jama'arsa,Zuriyar Yakubu za su yi farin ciki,Jama'ar Isra'ila za su yi murna.