5 A lokatan wahala zai kiyaye ni a inuwarsa,Zai kiyaye ni lafiya a Haikalinsa,Zai ɗora ni a kan dutse mai tsayi, ya kiyaye ni.
6 Ta haka zan ci nasara a kan magabtana da suke kewaye da ni.Da sowar farin ciki mai yawa zan miƙa sadakoki a Haikalinsa!Zan raira waƙa, in yabi Ubangiji!
7 Ka ji ni, ya Ubangiji, sa'ad da na ya yi kira gare ka!Ka yi mini jinƙai ka amsa mini!
8 Ka ce, “Zo wurina,”Zan kuwa zo gare ka, ya Ubangiji,
9 Kada ka ɓoye mini fuskarka, ya Ubangiji!Kada ka yi fushi da ni,Kada kuwa ka kori bawanka.Kai ne kake taimakona, tun dā ma,Kada ka bar ni, kada ka yashe ni,Ya Allahna, Mai Cetona!
10 Mai yiwuwa ne ubana da uwata su yashe ni,Amma Ubangiji zai lura da ni.
11 Ka koya mini abin da ya kamata in yi, ya Ubangiji,Ka bi da ni kan lafiyyiyar hanya,Domin ina da magabta da yawa.