11 Magabtana duka suna mini ba'a,Maƙwabtana sun raina ni,Waɗanda suka san ni kuwa suna jin tsorona,Sa'ad da suka gan ni a kan titi sukan guje mini.
12 Duk an manta da ni kamar matacce,Na zama kamar abin da aka jefar.
13 Na ji magabtana da yawa suna raɗa,Razana ta kewaye ni!Suna ƙulla maƙarƙashiya don su kashe ni.
14 Amma a gare ka na dogara, ya Ubangiji,Kai ne Allahna.
15 Kana lura da ni kullum,Ka cece ni daga magabtana,Daga waɗanda suke tsananta mini.
16 Ni, bawanka ne,Ka dube ni da alherinka,Ka cece ni saboda madawwamiyar ƙaunarka!
17 Ina kira gare ka, ya Ubangiji,Kada ka bari a ci nasara a kaina!Ka sa a ci nasara a kan mugaye,Ka sa su yi shiru a lahira.