12 Wahalai iri iri sun kewaye ni, har ba su ƙidayuwa!Alhakin zunubaina ya tarar da ni,Har ba na iya gani,Sun fi gashin kaina yawa, na karaya.
13 Ka cece ni, ya Allah,Ya Ubangiji, ka yi hanzari ka taimake ni!
14 Ka sa masu so su kashe ni,A ci nasara a kansu, su ruɗe!Ka sa waɗanda suke murna saboda wahalainaSu koma baya, su sha kunya!
15 Ka sa waɗanda suke mini ba'aSu razana sabili da faɗuwarsu!
16 Ka sa dukan waɗanda suke zuwa gare kaSu yi murna, su yi farin ciki!Ka sa waɗanda suke ƙaunar cetonkaKullayaumi su ce, “Allah da girma yake!”
17 Ba ni da ƙarfi, ba mataimaki,Ya Allah, ka zo wurina da hanzari.Kai ne mataimakina da Mai Cetona,Kada ka yi jinkiri, ya Ubangiji!