3 Ya koya mini raira sabuwar waƙa,Waƙar yabon Allahnmu.Da yawa idan suka ga wannan za su tsorata,Za su kuwa dogara ga Ubangiji.
4 Mai farin ciki ne mutumin da yake dogara ga Ubangiji,Wanda bai juya ga gumaka ba,Ko ya haɗa kai da masu sujada ga allolin karya.
5 Ka yi mana abubuwa masu yawa, ya Ubangiji Allahna.Ba wani kamarka!Idan na yi ƙoƙari in faɗe su duka,Sun fi ƙarfin in faɗa.
6 Ba ka bukatar baye-baye da hadayu,Ba ka so a miƙa maka hadayun ƙonawaNa dabbobi a bisa bagade ba,Ko baya-baye don a kawar da zunubai.A maimakon haka, ka ba ni kunnuwan da zan saurare ka.
7 Sai na amsa, “Ga ni, umarnanka zuwa gare niSuna a Littafin Shari'a.
8 Ina ƙaunar in aikata nufinka sosai, ya Allah!Ina riƙe da koyarwarka a zuciyata.”
9 A taron dukan jama'arka, ya Ubangiji,Na ba da albishir na cetonka.Ka sani ba zan fasa hurta shi ba.