1 Ubangiji mai girma ne,Dole kuwa a yabe shi da girmamawa a birnin Allahnmu,A kan tsattsarkan dutsensa.
2 Dutsen Sihiyona, dutse mai tsawo,Mai kyan gani ne na Allah,Birnin babban Sarki.Yakan kawo farin ciki ga dukan duniya!
3 Allah ya nuna akwai zaman lafiya a wurinsa,A kagarar birnin.
4 Sarakuna suka tattaru,Suka zo Dutsen Sihiyona,
5 Da suka gan shi sai suka yi mamaki,Suka tsorata suka gudu.
6 Tsoro ya kama su suka razana,Kamar mace wadda take gab da haihuwa.