25 Mawaƙa suna kan gaba, mabusa suna biye,A tsakiya kuwa 'yan mata suna kaɗa bandiri.
26 “Ku jama'ar Allah, ku yabe shi cikin taronku,Ku yabi Ubangiji, dukanku, ku zuriyar Isra'ila!”
27 Ga Biliyaminu mafi ƙanƙantaCikin kabilai, a kan gaba,Sa'an nan shugabannin Yahuza da ƙungiyarsu,Daga nan sai shugabannin Zabaluna da na Naftali suna biye da su.
28 Ka nuna ikonka, ya Allah,Ikon nan da ka nuna saboda mu.
29 Daga Haikalinka a Urushalima,Sarakuna sukan kawo maka kyautai.
30 Ka tsauta wa Masar, naman jejin nanMai zafin hali da yake cikin iwa,Ka tsauta wa sauran al'umma, taron bijiman nan da 'yan maruƙansu,Har dukansu su durƙusa, su miƙa maka azurfarsu.Ka warwatsar da jama'ar nanMasu son yin yaƙi!
31 Wakilai za su zo daga Masar,Habashawa za su miƙa hannuwansu sama,Su yi addu'a ga Allah.