3 Wahala mai yawa ta auko mini,Har ina gab da mutuwa.
4 Ina daidai da sauran mutanen da suke gab da mutuwa,Dukan ƙarfina ya ƙare.
5 An yashe ni a cikin matattu,Kamar waɗanda aka karkashe,Suna kuma kwance cikin kaburburansu,Waɗanda ka manta da su ɗungum,Waɗanda taimakonka ya yi musu nisa.
6 Ka jefar da ni cikin zurfin kabari,Da cikin rami mafi zurfi, mafi duhu.
7 Fushinka yana da nauyi a kaina,An turmushe ni a cikin tuƙuƙinka.
8 Ka sa abokaina su yashe ni,Ka sa sun ware ni.An kange ni, ba yadda zan kuɓuta.
9 Idanuna sun raunana saboda wahala.Ya Ubangiji, kowace rana ina kira gare ka,Ina ta da hannuwana zuwa gare ka da addu'a!