3 Ba magana ko kalma da aka hurta,Ba wani amon da aka ji,
4 Duk da haka muryarsu ta game duniya duka,Saƙonsu ya kai ko'ina a duniya.Allah ya kafa wa rana alfarwa a sararin sama,
5 Tana fitowa kamar ango yana taƙama daga gidansa,Kamar ɗan wasan da ya ƙosa ya yi tsere.
6 Takan fara daga wannan ƙarshen sararin sama, ta kewaye zuwa wancan.Ba abin da zai iya ɓuya daga zafinta.
7 Dokar Ubangiji cikakkiya ce,Tana wartsakar da rai.Umarnan Ubangiji abin dogara ne,Sukan ba da hikima ga wanda ba shi da ita.
8 Ka'idodin Ubangiji daidai suke,Waɗanda suke biyayya da su sun ji daɗi.Umarnan Ubangiji daidai suke,Sukan ba da fahimi ga zuciya.
9 Daidai ne a bauta wa Ubangiji,A ci gaba da yi har abada.Duk abin da Ubangiji ya hukunta daidai ne,A kullum hukuntan Ubangiji daidai suke.